NLC za ta tsunduma yajin aiki saboda cire tallafin man fetur

Rahotanni sun bayyana cewa kungiyar kwadago ta Najeriya NLC ta yi barazanar shiga yajin aikin gama gari a wata mai zuwa saboda tabarbarewar tattalin arziki da ake fama da shi sakamakon cire tallafin man fetur a kasar.

Kakakin kungiyar, Ben Upah, ne ya bayyana hakan a ranar Laraba, inda ya kara da cewa sun baiwa gwamnatin tarayya kwanaki bakwai don magance wannan batu.

In ba a manta ba dai Shugaba Bola Tinubu, a yayin rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayu, ya bayyana cire tallafin man fetur.

Ba zato ba tsammani matakin ya kara hauhawar farashin kayayyakin, wanda ya kara wa talakawa wahala.

A cewar Upah, ƙungiyar ta bayar da sanarwar yajin aikin a fadin kasar daga ranar 2 ga watan Agusta domin nuna rashin amincewa da cire tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi.

“Eh, za a fara yajin aikin a fadin kasar a ranar 2 ga watan Agusta 2023. Nan ba da jimawa ba za mu fitar da sanarwar hakan,” in ji Upah.

Hakan dai na zuwa ne sa’o’i kadan bayan kungiyar likitoci ta kasa (NARD) ta fara yajin aikin sai baba-ta-gani a kasar.

More News

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...