NDLEA ta kama wasu maniyyata da suka yi niyar safarar hodar ibilis zuwa ƙasar Saudiyya

Hukumar NDLEA dake yaƙi da hana sha da kuma fataucin miyagun ƙwayoyi ta kama wasu maniyyata su huɗu ɗauke da wata hoda da ake kyautata zaton hodar ibilis ce.

Mutanen da aka kama sun haɗa da Usman Kamorudeen, Olasunkanmi Owolabi, Fatai Yekini, da kuma Ayinla Kemi.

A wata sanarwa ranar Alhamis, Femi Babafemi mai magana da yawun hukumar ta NDLEA ya ce an kama mutanen ne a ɗakin wani otal lokacin da suke haɗiye ƙunshin ƙwayar hodar ibilis ɗin gabanin tashin su zuwa ƙasar Saudiya a ranar Laraba.

“Mutane huɗun da ake zargi an ajiye su ne a wani otal inda aka shirya musu ƙunshin ƙwayar hodar ibilis guda 200 mai nauyin kilogiram 220 domin su haɗiye a lokacin da jami’an NDLEA suka farma ɗakin,”

Sanarwar ta ƙara da cewa an gano ƙunshi 100 a kowane ɗaki inda mutane biyu za su haɗiye 100 kowannensu.

Tuni shugaban hukumar ta NDLEA, Buba Marwa ya yabawa jami’an hukumar na jihar Lagos kan kamen da suka yi.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...