Nan bada jimawa za a kawo karshen rashin wutar lantarki a Kebbi

Gwamnatin jihar Kebbi ta roki mazauna jihar da su kara hakuri inda ta ce rashin wutar lantarki da ake fuskanta a jihar zai zo karshe nan bada jimawa.

A ranar 14 ga watan Satumba gobara ta kama a tashar wutar lantarki inda ta kone babbar na’urar taransifoma 330KV mallakin kamfanin rarraba hasken wutar lantarki na KEDCO dake birnin Kebbi.

Gobarar ta jefa jihohin Sokoto, Kebbi da kuma wasu sassan jihar Zamafara a cikin duhu.

Yakubu Bala Tafida sakataren gwamnatin jihar, shi ne ya bada tabbacin a ranar Asabar lokacin da ya ziyarci karamar tashar wutar lantarki ta hukumar TCN dake birnin Kebbi.

Sakataren ya ce ya ziyarci wurin ne a madadin gwamnan jihar wanda ya umarce shi ya saka ido akan aikin “saboda baya son al’ummarsa su cigaba da zama cikin duhu.”

Ya bayyana gamsuwarsa da aikin da aka yi kawo yanzu a kokarin dawo da wutar lantarki jihar.

More News

Hukumar NMDPRA ta rufe wani gidan mai da ya karkatar da tankar man fetur 18

Hukumar NMDPRA dake lura da tacewa tare rarraba man fetur da iskar gas ta rufe gidan man Botoson Oil and Gas LTD dake jihar...

Jirgin saman kamfanin Xejet ya zame daga kan titin filin jirgin saman Lagos

A ranar Asabar ne wani jirgin sama mallakin kamfanin Xejet ya zame daga kan titin filin jirgin saman Murtala Muhammad dake Lagos. Hukumar NSIB dake...

Lauya ya nemi kotu ta bashi mako 4 ya nemo inda Yahaya Bello ya É“uya

Abdulwahab Mohammed babban lauyan tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya nemi babbar kotun tarayya dake Abuja da ta bashi makonni huÉ—u domin ya...

ÆŠalibai 9 aka tabbatar da yin garkuwa da su daga jami’an jihar Kogi

Gwamnatin jihar Kogi ta tabbatar da cewa É—alibai 9 aka tabbatar sun É“ace bayan da wasu Æ´an bindiga suka kai farmaki Jami'ar Kimiya da...