
Gwamnatin jihar Kebbi ta roki mazauna jihar da su kara hakuri inda ta ce rashin wutar lantarki da ake fuskanta a jihar zai zo karshe nan bada jimawa.
A ranar 14 ga watan Satumba gobara ta kama a tashar wutar lantarki inda ta kone babbar na’urar taransifoma 330KV mallakin kamfanin rarraba hasken wutar lantarki na KEDCO dake birnin Kebbi.
Gobarar ta jefa jihohin Sokoto, Kebbi da kuma wasu sassan jihar Zamafara a cikin duhu.
Yakubu Bala Tafida sakataren gwamnatin jihar, shi ne ya bada tabbacin a ranar Asabar lokacin da ya ziyarci karamar tashar wutar lantarki ta hukumar TCN dake birnin Kebbi.
Sakataren ya ce ya ziyarci wurin ne a madadin gwamnan jihar wanda ya umarce shi ya saka ido akan aikin “saboda baya son al’ummarsa su cigaba da zama cikin duhu.”
Ya bayyana gamsuwarsa da aikin da aka yi kawo yanzu a kokarin dawo da wutar lantarki jihar.