Namadi Sambo zai jagoranci kwamitin sake gina masallacin Juma’a na Zaria da ya ruguje

Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya kafa wani kwamitin kwararru mai mambobi 11 kan sake gina babban masallacin Juma’a na Zaria da ya rushe.

A wata sanarwa da Abdullahi Aliyu Kwarbai mai magana da yawun masarautar ya ce tsohon mataimakin shugaban kasa kuma Sardaunan Zazzau, Arc Namadi Sambo shi ne zai kasance shugaban kwamitin a yayin da Arch. Ibrahim Waziri zai zamo sakataren kwamitin.

Sanarwar ta kara da cewa “mambobin kwamitin sun haɗa da Arch. Abubakar Abdulkadir, Professor Kabir Bala, Vice Chancellor, ABU, Arch. Muhammadu Aminu Idris, Sheikh Dr. Hayatuddeen, Arch. Gambo Hamza da TPL Bello Nuhu Yakubu.

“Sauran su ne Bld. Lawal Magaji, Arch. Isa A. A and Arch. Haruna Abubakar Bamalli.”

Idan za a iya tunawa a ranar Juma’a 11 ga watan Agusta na shekerar 2023 wani sashe babban masallacin Juma’a na masarautar Zazzau ya ruguzo kan masallata.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...