Najeriya ta yanke ba wa Nijar wutar lantarki

A ranar Larabar da ta gabata ne aka dakatar da samar da wutar lantarki daga Najeriya zuwa jamhuriyar Nijar, yayin da kasashen yammacin Afirka ke kara kakabawa makwabciyar kasar takunkumi.

A ranar Lahadin da ta gabata ne kungiyar ECOWAS karkashin jagorancin shugaban Najeriya Bola Tinubu ta yanke shawarar sanya takunkumi kan sojojin Nijar da suka hambarar da zaɓaɓɓen shugaban kasar Mohamed Bazoum a makon jiya.

A ranar 26 ga watan Yuli, jami’an tsaron fadar shugaban kasa suka kama Bazoum tare da ayyana shi cewa sun tsige shi.

Baya ga maido da wa’adin mako guda ga tsarin mulki da kuma dakatar da hada-hadar kudi da Nijar, ECOWAS ta ba da umarnin dakatar da “dukkan hada-hadar, gami da hada-hadar makamashi da ita.”

More News

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...