Najeriya ta nemi taimakon Jamus don yaƙi da ta’addanci

A ranar Lahadi ne shugaba Bola Tinubu ya nemi goyon bayan shugaban gwamnatin Jamus Olaf Scholz kan yaki da ta’addanci a Najeriya.

Mista Tinubu ya miƙa wannan bukata ne a wata ganawa da ya yi da shugaban gwamnatin Jamus a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja ranar Lahadi.

“Muna yaki da ta’addanci kuma hakan yana inganta. Har yanzu muna buƙatar ƙarin tallafi a wannan yanki. Kuma don mu sami damar dorewar dimokuradiyya, bin doka da ’yanci ga jama’armu, muna bukatar mu yi gwagwarmayar tabbatar da dimokuradiyya.

“Kuma dole ne dimokuradiyya ta yi nasara a kowane lokaci domin mu cimma burinmu a Afirka. Shi ya sa ziyararku a wannan karon ta fi zama dole.

“Za ku lura, ba na buƙatar yin magana game da matsalolin daban-daban da ke faruwa a yankin Sahel na Afirka. Kun ga kuma kun lura da juyin mulkin da aka yi a Guinea da kwanan nan a Jamhuriyar Nijar,” in ji Tinubu

Najeriya dai na fama da matsaloli iri-iri tun bayan bayan dawowarta ta farkon dimokuraɗiyya.

More from this stream

Recomended