Najeriya na fuskantar mummunan matsin tattalin arziki da ba ta taɓa fuskanta ba—Sanata Abdullahi

Shugaban kwamitin majalisar dattawa kan tsare-tsare da harkokin tattalin arziki, Yahaya Abdullahi, ya ce Najeriya na fuskantar matsalar tattalin arziki mafi muni a tarihin wanzuwarta.

Abdullahi, wanda ke wakiltar mazabar Kebbi ta Kudu a jihar Kebbi, ya bayyana hakan ne a taron kaddamar da kwamitin majalisar a ranar Laraba.

Wannan dai kamar yadda ya ce akwai bukatar majalisar ta yi mu’amala da bangaren zartarwa a wani yunkuri na sake farfado da tattalin arzikin kasar da kuma dawo da shi kan turba.

Abdullahi ya kuma bukaci kwamitocin tsare-tsare na kasa a cikin majalisar da majalisar dattawa da su yi duk mai yiwuwa a cikin shekaru hudu don cimma burin da aka tsara na juya tattalin arzikin kasar, tare da ba da shawara ga hukuma.

More News

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...