Najeriya Na Ci Gaba Da Shari’ar Masu Hannu A Hare-Haren ‘Yan Ta-da-ƙayar-Baya

Najeriya na ci gaba da gudanar da shari’a kan fiye da mutum 500 da ake zarginsu da hannu a hare-haren ‘yan ta-da-ƙayar-baya da suka yi sanadin mutuwar dubban mutane, a ɗaya daga cikin manyan shari’o’in ta’addanci a ƙasar.

Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi, ya bayyana cewa shari’ar ta fara ne da gurfanar da mutum 227 a gaban alƙalai guda goma. Ana zargin waɗannan mutane da kai hare-hare a akasari a sassan arewacin Najeriya, inda ayyukan tarzoma suka yi sanadin kashe fiye da mutum dubu biyu da raba ɗumbin wasu daga gidajensu.

Sauran wadanda ake tuhuma na fuskantar zargin goyon bayan ‘yan ta-da-ƙayar-baya ta hanyar ba su kuɗaɗe, makamai da sauran kayan buƙatun rayuwa. Ministan ya ce girman wannan shari’a na nuna ƙudurin gwamnati na ganin an bi ƙa’ida wajen hukunta masu hannu a ta’addanci.

An tsaurara matakan tsaro da suka haɗa da sojoji, ‘yan sanda da jami’an leƙen asiri. Masu sa-ido na duniya, ciki har da ƙungiyoyin kare ‘yancin ɗan’adam da ƙungiyar lauyoyi ta Najeriya, sun halarci kotun.

A ranar Talata, an yanke wa mutum biyar hukuncin ɗaurin shekaru daban-daban a gidan yari bayan sun amsa laifi kan sayar da dabbobi, kai kayan abinci da tsegunta bayanai ga ‘yan ta-da-ƙayar-baya. Hukumar shari’a ta ce za a ci gaba da gudanar da shari’o’in kashi-kashi, lamarin da ke nuna an ɗauki mataki mai ƙarfi kan rikicin ta-da-ƙayar-bayan da ya dade yana addabar sassan Najeriya.

More from this stream

Recomended