Najeriya da Cuba za su ƙara ƙulla alaƙa mai ƙarfi

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima a ranar Alhamis ya bayyana bukatar gwamnatin shugaba Bola Tinubu na kara zurfafa dangantakar da ke tsakanin kasar Najeriya da Jamhuriyar Cuba.

Daraktan yada labarai na ofishin mataimakin shugaban kasar, Olusola Abiola, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce Shettima ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar ban girma da ya kai wa mataimakin shugaban kasar Cuba, Salvador Valdez Mesa a fadar De Revolution, Havana.

A halin yanzu Mista Shettima yana kasar Cuba ne domin wakiltar Tinubu a taron shugabannin kasashen G77+ na kasar Sin a birnin Havana na kasar Cuba, wanda ake gudanarwa daga ranar 15 zuwa 17 ga watan Satumba.

Ya kara da cewa, “Muna matukar girmama kasar Cuba, musamman irin sadaukarwar da kuka yi mana a Afirka.”

Yayin da yake yabawa da dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, Mista Shettima ya jaddada bukatar kasashen biyu su sake kulla alaka a nan gaba.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...