NAFDAC ta hana shigo da Indomie saboda tana jawo cutar daji

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa (NAFDAC) ta haramta shigo da taliyar Indomie zuwa Najeriya.

A wata zantawa da ta yi da manema labarai a ranar Litinin, Darakta Janar na Hukumar, Farfesa Mojisola Adeyeye, ta bayyana hakan.

Hukumar ta NAFDAC ta dauki matakin ne biyo bayan wani bincike da hukumomin Taiwan da na Malaysia suka gudanar, inda ta ce an gano sinadarin ethylene oxide mai haddasa cutar daji a cikin taliyar.

Shugaban hukumar ta bayyana cewa akwai abin dubawa al’amarin ethylene oxide kuma tuni aka tuntubi daraktan kula da ayyukan dakin gwaje-gwajen abinci kuma yana aiki kan hanyar tantancewa game wannan batu.

More News

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

Ƴan sanda sun kama masu garkuwa da mutane da suka yi bacci a lokacin da suke tsare da mutanen da suka sace

Jami'an Æ´an sanda sun samu nasarar kama wasu masu garkuwa da mutane bayan da suka buge da sharar bacci a lokacin da suke tsare...

Gwamnatin Adamawa Ta Ƙara Hutun Ɗaliban Makarantu Saboda Annobar Cutar Ƙyanda

Gwamnatin jihar Adamawa ta tsawaita lokacin komawar É—aliban jihar makarantunsu domin fara  zangon karatu na uku saboda annobar cutar Æ™yanda. A wata sanarwa ranar Litinin,...

Sojan Jamhuriyar Nijar sun kama Gawurtaccen ÆŠan Fashin dajin Najeriya Kachalla Mai Daji

Dakarun sojan Jamhuriyar Nijar sun samu nasara kama gawurtaccen É—an fashin dajin nan mai suna Kachalla Mai Daji a garin Illela dake kan iyakar...