WASHINGTON, DC —
Wakilin Muryar Amurka Abdulwahab Muhammad ya tattauna da dan Majalisar Dokokin jihar Bauchi, Abdulkadir Umar Dewu dake garin Kirfi domin bin diddigin lamarin, sai dai ya ce basu da masaniyar yawan mutanen da ke cikin kwale kwalen, an kuma kamanta yawan wadanda suka mutu 30, amma ba a tabbabtar ba.
Ya kara da cewa, har ya zuwa wannan rahoto jama’a na ta zuwa neman ‘yan uwansu da suka shiga wannan kwale kwale.
Ya bada shawarar cewa dole gwmanatin tarayya to shigo don ta taimaka wa karamar hukumar Game da wannan matsala, a kuma samo masu sauki. Ya ce wadanda suka iya ruwa a jikin su, sun fito da rai, amma dayawa sun rasa rayukansu.








