![](https://arewa.ng/storage/2020/08/Mutane-9-sun-mutu-a-hatsarin-kwale-kwale-a-Sokoto-–-AREWA-News.jpg)
Mutane 9 ake fargabar sun mutu bayan da kwale-kwalen da suke tafiya a ciki ya kife da su a kauyen Birjingo dake karamar hukumar Goronyo ta jihar.
Jaridar Daily Trust ta gano cewa yawancin mutanen dake cikin jirgin mata ne da kananan yara da kuma wata budurwa da ake shirin yiwa aure da suke tare da mahaifiyarta.
Bayanai sun bayyana cewa jirgin na dauke da mutane sama da 30 lokacin da lamarin ya faru.
An ce fasinjojin na kan hanyarsu ne ta zuwa gonar shinkafa dake tsallaken kogin inda suke aikin kwadago.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Isa Muhammad kansilan dake wakiltar mazabar Birjingo,ya ce hatsarin ya faru ne da misalin karfe 8 na safiyar ranar Laraba.
Dagacin kauyen Birjingo, Alhaji Shehu Dangaladima ya ce jirgin ya nutse ne saboda an dauki mutane fiye da ka’ida a ciki.