Mutane 9 sun mutu a hatsarin kwale-kwale a Sokoto – AREWA News

Mutane 9 ake fargabar sun mutu bayan da kwale-kwalen da suke tafiya a ciki ya kife da su a kauyen Birjingo dake karamar hukumar Goronyo ta jihar.

Jaridar Daily Trust ta gano cewa yawancin mutanen dake cikin jirgin mata ne da kananan yara da kuma wata budurwa da ake shirin yiwa aure da suke tare da mahaifiyarta.

Bayanai sun bayyana cewa jirgin na dauke da mutane sama da 30 lokacin da lamarin ya faru.

An ce fasinjojin na kan hanyarsu ne ta zuwa gonar shinkafa dake tsallaken kogin inda suke aikin kwadago.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Isa Muhammad kansilan dake wakiltar mazabar Birjingo,ya ce hatsarin ya faru ne da misalin karfe 8 na safiyar ranar Laraba.

Dagacin kauyen Birjingo, Alhaji Shehu Dangaladima ya ce jirgin ya nutse ne saboda an dauki mutane fiye da ka’ida a ciki.

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]