Mutane 6 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Jihar Niger

Matafiya da basu gaza shida ba ne aka bada rahoton sun mutu bayan da wani jirgin ruwan fasinja ya nutse a kogin Zamare a karamar hukumar Agwara ta jihar Niger.

Lamarin ya faru ne a ranar Litinin lokacin da matafiya da yawancinsu manoma ne suke zuwa jihar Kebbi.

Mazauna garin sun fadawa jaridar Daily Trust cewa an gano gawar É—aya daga cikin matafiyan a yayin da ake cigaba da aikin nemo sauran.

Jirgin na dauke da mutane sama da 20 ciki har da mata da kananan yara ya kuma kife ne bayan da injinsa ya lalace a tsakiyar ruwa kamar yadda ake shedawa wakilin jaridar Daily Trust.

Shugaban hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Niger, Garba Salihu ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya ce hukumar bata samu cikakken rahoton kan abin da ya faru ba.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...