Musulmi a Zaria sun yi taron addu’o’i saboda mummunan halin matsi da Najeriya ke ciki

Musulmi a garin Zaria na jihar Kaduna, sun gudanar da addu’a ta musamman domin neman taimakon Allah kan halin da ‘yan Najeriya ke ciki a halin yanzu.

Sallar ta musamman da aka gudanar a filin Sallar Idi na Mallawa da ke Zariya ta samu halartar mata da maza daga sassa daban-daban na garin.

Da yake jagorantar addu’ar ta musamman, babban limamin masallacin Juma’a na Bakin Kasuwa (Tudun Wada), Malam Muhammadu Sani Labudda, ya bayyana wahalhalun da ake ciki a yanzu a matsayin wanda ba za a iya jurewa ba wanda ke bukatar taimakon Allah.

Ya ce halin da ake ciki a kasar nan na da matukar wahala da ke bukatar addu’o’i na gama-gari musamman ganin yadda farashin kayayyakin masarufi ke tashi a ranar da Musulmi ke gab da shiga watan Ramadan.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...