Musulmi a Zaria sun yi taron addu’o’i saboda mummunan halin matsi da Najeriya ke ciki

Musulmi a garin Zaria na jihar Kaduna, sun gudanar da addu’a ta musamman domin neman taimakon Allah kan halin da ‘yan Najeriya ke ciki a halin yanzu.

Sallar ta musamman da aka gudanar a filin Sallar Idi na Mallawa da ke Zariya ta samu halartar mata da maza daga sassa daban-daban na garin.

Da yake jagorantar addu’ar ta musamman, babban limamin masallacin Juma’a na Bakin Kasuwa (Tudun Wada), Malam Muhammadu Sani Labudda, ya bayyana wahalhalun da ake ciki a yanzu a matsayin wanda ba za a iya jurewa ba wanda ke bukatar taimakon Allah.

Ya ce halin da ake ciki a kasar nan na da matukar wahala da ke bukatar addu’o’i na gama-gari musamman ganin yadda farashin kayayyakin masarufi ke tashi a ranar da Musulmi ke gab da shiga watan Ramadan.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...