Murja Ibrahim Kunya ta bayyana cewa ba ta da sha’awar shirin auren zaurawa da za a yi a Kano wanda hukumar Hisbah ta jihar ta shirya.
Ana sa ran shirin zai laƙume kusan naira biliyan 1 wa gwamnatin jihar.
A kwanakin baya ne gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir ya fito bainar jama’a ya bayyana aniyarsa ta aurar da Murja Ibrahim, fitacciyar jarumar TikTok kuma mai goyon bayansa.
Shirin wanda tun asali gwamnatin Kwankwaso ne ta fara aiwatar da shi, daga baya kuma gwamnatin Ganduje ta dakatar da shi, gwamnatin Abba Kabir ce ta dawo da shi.
Dangane da wannan tayin, Murja ta ki amincewa, inda ta jaddada cewa goyon bayanta ga gwamnan ba wai don neman abin duniya bane.
Murja ta kara da cewa ita mabiyiya ce mai biyayya ga kungiyar Kwankwasiyya karkashin jagorancin Dr. Rabiu Kwankwaso, wadda ke goyon bayan takarar Abba ta gwamna.