Mun kashe kusan naira biliyan 1 saboda tura yara karatun liktanci a Misra—Gwamnan Katsina

Gwamna Dikko Radda na jihar Katsina ya ce gwamnatinsa ta kashe Naira miliyan 900 ga wasu dalibai marasa galihu 41 don yin karatun digiri na farko a fannin likitanci, MBBS, a jami’ar Al-Nahda da ke kasar Masar.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Litinin a wajen kaddamar da tallafin karatu na kasashen waje na MBBS a Katsina.

Ya ce an zabo dalibai marasa galihu ne bisa cancanta, bayan da aka gudanar da jarrabawa ga masu sha’awar shiga makarantun gaba da sakandire na gwamnati a jihar.

A cewarsa, kudaden za su isa a biya dukkan kudaden karatunsu da sauran bukatunsu na tsawon shekaru biyu.

Ya ce gwamnatin jihar ta fara shirin bai wa daliban MBBS tallafin karatu daga kasashen waje domin magance karancin likitocin jihar.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu É—aliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karÉ“ar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...