Mun kashe kusan naira biliyan 1 saboda tura yara karatun liktanci a Misra—Gwamnan Katsina

Gwamna Dikko Radda na jihar Katsina ya ce gwamnatinsa ta kashe Naira miliyan 900 ga wasu dalibai marasa galihu 41 don yin karatun digiri na farko a fannin likitanci, MBBS, a jami’ar Al-Nahda da ke kasar Masar.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Litinin a wajen kaddamar da tallafin karatu na kasashen waje na MBBS a Katsina.

Ya ce an zabo dalibai marasa galihu ne bisa cancanta, bayan da aka gudanar da jarrabawa ga masu sha’awar shiga makarantun gaba da sakandire na gwamnati a jihar.

A cewarsa, kudaden za su isa a biya dukkan kudaden karatunsu da sauran bukatunsu na tsawon shekaru biyu.

Ya ce gwamnatin jihar ta fara shirin bai wa daliban MBBS tallafin karatu daga kasashen waje domin magance karancin likitocin jihar.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]