Mun gyara kilomita 102 na titunan jihohin Gombe da Bauchi da Adamawa cikin wata 2—FERMA

Hukumar kula da tituna ta tarayya (FERMA) ta ce ta gyara sama da kilomita 102 na hanyoyin da suka samu matsala a fadin jihohi uku na arewa maso gabas na Adamawa, Bauchi da Gombe a cikin watanni biyun da suka gabata.

Jagoran tawagar, Dr Mansur Hamma-Adama, wanda ya bayyana hakan bayan ya duba wani yanki da aka gyara a Gombe a ranar Asabar, ya ce an gyara hanyoyin da suka lalace ta hanyar ‘Operation Connect to Your Destined in North East II sub-Region.

Ana gudanar da shirin kowace shekara a ƙarshen shekara don taimaka wa masu ababen hawa da ke dawowa don hutu kuma don samun sauƙi a lokacin bukukuwan Kirsimeti.

A cewarsa, sashen ma’aikata na FERMA ne ke gudanar da aikin a kowace shiyya na ƙasar.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]