Mun gyara kilomita 102 na titunan jihohin Gombe da Bauchi da Adamawa cikin wata 2—FERMA

Hukumar kula da tituna ta tarayya (FERMA) ta ce ta gyara sama da kilomita 102 na hanyoyin da suka samu matsala a fadin jihohi uku na arewa maso gabas na Adamawa, Bauchi da Gombe a cikin watanni biyun da suka gabata.

Jagoran tawagar, Dr Mansur Hamma-Adama, wanda ya bayyana hakan bayan ya duba wani yanki da aka gyara a Gombe a ranar Asabar, ya ce an gyara hanyoyin da suka lalace ta hanyar ‘Operation Connect to Your Destined in North East II sub-Region.

Ana gudanar da shirin kowace shekara a ƙarshen shekara don taimaka wa masu ababen hawa da ke dawowa don hutu kuma don samun sauƙi a lokacin bukukuwan Kirsimeti.

A cewarsa, sashen ma’aikata na FERMA ne ke gudanar da aikin a kowace shiyya na ƙasar.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...