Mun ayyana ranar Litinin a matsayin ranar hutu—Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Litinin 29 ga watan Mayun 2023 a matsayin ranar hutu a fadin kasar nan a hukumance.

Matakin dai shi ne baiwa dukkan ‘yan Najeriya damar gudanar da bikin rantsar da zababben shugaban kasar karo na 16 bisa tafarkin dimokradiyya.

Dr Shuiab Belgore, babban sakatare a ma’aikatar harkokin cikin gidan kasar ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a. Ya kara da cewa ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola ne ya bayyana hakan a madadin gwamnatin tarayya.

Aregbesola ya mika sakon fatan alheri ga daukacin ‘yan Najeriya kan wannan gagarumin biki tare da yaba musu kan yadda suka yi imani da dimokuradiyya.

Wannan imanin ya bayyana a zaben da aka yi a fadin kasar wanda ya sa aka rantsar da shugaban kasa da mataimakinsa, da kuma a dukkan zabukan kasar.

Ya kuma yi kira ga kowa da kowa da ya yi amfani da wannan hutun don yin tunani a kan tafiyar dimokuradiyyar al’umma da makomarta a karkashin sabon shugabanci.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]