Mun ayyana ranar Litinin a matsayin ranar hutu—Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Litinin 29 ga watan Mayun 2023 a matsayin ranar hutu a fadin kasar nan a hukumance.

Matakin dai shi ne baiwa dukkan ‘yan Najeriya damar gudanar da bikin rantsar da zababben shugaban kasar karo na 16 bisa tafarkin dimokradiyya.

Dr Shuiab Belgore, babban sakatare a ma’aikatar harkokin cikin gidan kasar ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a. Ya kara da cewa ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola ne ya bayyana hakan a madadin gwamnatin tarayya.

Aregbesola ya mika sakon fatan alheri ga daukacin ‘yan Najeriya kan wannan gagarumin biki tare da yaba musu kan yadda suka yi imani da dimokuradiyya.

Wannan imanin ya bayyana a zaben da aka yi a fadin kasar wanda ya sa aka rantsar da shugaban kasa da mataimakinsa, da kuma a dukkan zabukan kasar.

Ya kuma yi kira ga kowa da kowa da ya yi amfani da wannan hutun don yin tunani a kan tafiyar dimokuradiyyar al’umma da makomarta a karkashin sabon shugabanci.

More News

An Jikkata Jami’an Tsaro A Harin Da Ƴan Bindiga Su ka Kai Wa Ayarin Motocin Yahaya Bello

A jikkata wasu jami'an tsaro a wani hari da yan bindiga su ka kai kan jerin ayarin motocin gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ranar...

Bala Muhammad ya zama shugaban gwamnonin jam’iyyar PDP

An zaɓi gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad a matsayin sabon shugaban kungiyar gwamnonin jam'iyyar PDP. Siminalayi Fabura zaɓaɓɓen gwamnan jihar Rivers shi ne mataimakin shugaban...

Za mu sake bitar mafi karancin albashi a Najeriya—Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya yi alkawarin sake nazarin mafi karancin albashin ma’aikata domin dacewa da yanayin tattalin arzikin kasar nan. A cewarsa, akwai bukatar...

EFCC na zargin tsohuwar ministar mata a mulkin Buhari da karkatar da naira biliyan 2

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta'annati ta titsiye tsohuwar ministar harkokin mata Pauline Tallen kan zargin azurta kai ta...