Mummunan hatsarin mota ya hallaka mutane 16 a hanyar Kano zuwa Kaduna

Hukumar Kiyaye Haɗɗura ta Ƙasa (FRSC) reshen jihar Kaduna ta ce mutane 16 ne suka mutu yayin da wasu hudu suka jikkata a wani hatsarin mota da ya afku a hanyar Kano zuwa Kaduna ranar Lahadi da misalin karfe 11:20 na safe.

Kwamandan shiyyar Kaduna, Kabir Nadabo, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya cewa, hatsarin ya afku ne a mahadar Taban Sani dake Tashar Yari kan hanyar Kano zuwa Kaduna.

Nadabo ya ce, “mummunan hatsarin motan ya hada da wata mota kirar Toyota Bus, mai lamba TRB 674ZG, wadda ta taso daga jihar Kano zuwa Makurdi ta jihar Benue, ya kuma bayyana cewa hatsarin ya faru ne sakamakon gudun wuce gona da iri da direban ya yi, wanda ya sa motar ta faɗa cikin rami.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...