Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi sani da Sunday Igboho, bisa zargin yi wa Fulani barazana a wani faifan bidiyo.

A ranar Litinin, dan a-waren ya shaida wa magoya bayansa cewa kada su jira gwamnatin kasar kafin ta dauki matakin yaki da Fulani makiyaya, wadanda ya yi zargin suna hana manoman yankin shiga gonakinsu a yankin Kudu maso Yamma.

“Wannan yanki ne namu. Mu kubutar da kanmu daga hannun Fulani. Ya kamata mu sanya tsaro a duk ƙasar Yarbawa. Ba mu buƙatar jiran kowa, har da gwamnati. Idan da gaske muke yi , bai kamata mu jira gwamnati ba, in ba haka ba Fulani za su ƙwace filayenmu gaba daya. Ya kamata mu kasance da haɗin kai. Wadanne gonaki ne muke da su kuma a kasar Yarbawa?  Za mu iya zuwa gona a yanzu?”, Mista Igboho ya ce.

Da yake mayar da martani ga sanarwar, shugaban kungiyar ta MACBAN na kasa, Baba Othman Ngelzarma, ya yi kira da a kama Mista Igboho tare da gurfanar da shi a gaban kuliya saboda ya yi “kalamai na cin amanar ƙasa.”

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...