Ministan tsaro Badaru ya yaba wa gwamnan Zamfara saboda tallafa wa aikin soji a jihar

Ministan Tsaro, Mohammed Abubakar Badaru, ya jinjina wa Gwamna Dauda Lawal bisa jajircewarsa da ci gaba da tallafa wa ayyukan soji a Jihar Zamfara.

Ministan ya yi wannan furuci ne a ranar Alhamis lokacin da ya kai wa gwamnan ziyara a fadar gwamnatin Jihar Zamfara. Ya kuma ziyarci hedikwatar hadin gwiwar rundunar Fansar Yamma da ke Gusau, inda ya umarci dakarun da su kama fitaccen dan ta’adda, Bello Turji.

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa manufar ziyarar ministan ita ce inganta hadin kai tsakanin gwamnatin jihar da ma’aikatar tsaro.

Sanarwar ta kara da cewa an tattauna batutuwan da suka shafi tsaro tsakanin ministan da gwamnan a matsayin ci gaba da taron da aka yi a farkon makon nan tsakanin Mr Badaru da Mr Lawal tare da takwaransa na Jihar Katsina, Dikko Radda, a ma’aikatar tsaro da ke Abuja.

More News

An kama mutane biyu  masu garkuwa da mutane a jihar Kogi

Wasu É“atagari biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne jami'an Æ´an sanda da haÉ—in gwiwar Æ´an bijilante suka kama a garin Ibobo-Abocho...

Jirgi mai saukar ungulu ya yi hatsari a Akwa Ibom

Wasu ma'aikatan kamfanin haƙar man fetur su 6 da kuma matuƙan jirgi su biyu su mutu a wani hatsarin jirgi mai saukar ungulu a...

Tinibu ya aikawa da majalisar dattawa sunaye 7 na ministocin da zai naɗa

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi kira ga majalisar dattawa da ta tabbatar da sunayen mutane 7 da ya tura majalisar da zai...

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...