Ministan lafiya ya ziyarci Duduwale

[ad_1]








Ministan lafiya Farfesa Isaac Adewale ya ziyarci, Abubakar Duduwale mutumin da ya yi tattaki daga Yola zuwa Abuja domin halartar bikin rantsar da shugaban kasa Muhammad Buhari a shekarar 2015.

Adewale ya ziyarci Duduwale wanda yanzu haka yake jiya a Cibiyar Kula Da Lafiya ta Tarayya dake Yola babban birnin jihar Adamawa, sakamakon ciwon kafa da yake fama da shi.

Ya yi alkawarin tabbatar da cewa Duduwale ya samu cikakkiyar lafiya.

Ministan ya sanar da haka cikin wani sakon Twitter da wallafa ɗauke da hoton Duduwale.

“Na ziyarci Abubakar Duduwale mutumin da yayi tattaki daga Yola zuwa Abuja don halartar bikin rantsar da shugaban kasa Muhammad Buhari a shekarar 2015 amma yanzu yana fama da jiyar rauni a kafarsa a Cibiyar Kula Da Lafiya ta Tarayya dake Yola.Zamu tabbatar da ya samu lafiya.”




[ad_2]

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...