Me ya sa gwamnoni ke adawa da cin gashin kan majalisar jiha?

Gwamnonin arewa

Hakkin mallakar hoto
@GovKaduna

Image caption

Gwamnoni sun ce dokar ta saɓawa kundin tsarin mulki

Batun ba majalisar dokoki da É“angaren shari’a a jihohi ‘Æ´ancin cin gashin kai a Najeriya na neman tayar da Æ™ura tsakanin shugaban Æ™asa da kuma gwamnoni.

A ranar 22 ga watan Mayu ne Shugaba Buhari ya rattaba hannu kan wata doka da ake kira Executive Order 10 da ta ba Æ´an majalisar dokoki da kotuna Æ´ancin cin gashin kai.

Shugaban kuma ya umarci ofishin babban akanta na Æ™asar da ya cire wa duk jihar da ta ci gaba da rike wa majalisar dokoki da bangaren shari’a kuÉ—in da ta rike daga kasonta na wata.

Sai dai kuma gwamnonin jihohin Najeriya 36 sun nuna rashin amincewa da dokar da shugaba Buhari ya sanya wa hannu, inda suka ce ƙudirin ya saɓa wa sashe na 121 na kundin tsarin mulki na 1999.

Dokar na nufin za a ware wa majalisun dokoki na jiha da É“angaren shari’a kudadensu a kasafin kuÉ—i, inda za su yi wa kansu kasafin kuÉ—i kan dukkanin abubuwan da suke buÆ™ata, matakin da gwamnoni ba sa so.

Bayan wani taro da suka yi kan batun ranar Juma’ar da ta gabata, gwamnonin sun cimma matsayar Æ™alubalantar matakin kuma rahotanni sun ce shugaban Æ™ungiyar gwamnonin – Gwamna Kayode Fayemi na Jihar Ekiti – ya gana da Buhari da kuma ministan shara’a kan batun.

Ƙungiyoyin Æ™wadago da ‘Æ´an Najeriya da dama sun yaba da matakin shugaban Æ™asar na amincewa da dokar wadda ake ganin za ta ba Æ´an majalisar dokokin jiha Æ´anci waÉ—anda ake ganin sun koma Æ´an amshin shatan gwamnonin duk da Æ™arfin da kundin tsarin mulki ya ba Æ´an majalisar jihar.

Yanzu duk kuɗaɗen da gwamnatocin jihohi suka karɓa daga kason asusun Gwamnatin Tarayya ko abin da suke samu na kuɗaɗen shiga dole su raba wa sauran ɓangarorin gwamnati nasu kason.

Kuma dokar ta ba Babban Akanta na Ƙasa damar zare kuÉ—aÉ—en duk jihar da gwamnanta ya Æ™i cire wa É“angaren majalisar dokoki da shari’a nasu kason.

Dokar dai na son daidaita ƙarfin da kundin tsarin mulki ya ba ko wane ɓangare na gwamnati a matakin jiha, musamman duba da ƙarfin da gwamnoni ke da shi a Najeriya.

Tun kafa jamhuriyya ta huɗu ake ganin gwamnoni sun ƙara wa kansu ƙarfin da ke danne sauran ɓangarorin gwamnati, duk da ƴancin da kundin tsarin mulki ya ba su.

Hakkin mallakar hoto
Buhari Sallau

Image caption

Gwamnoni na iya garzayawa kotu domin ƙalubalantar dokar

Dokar na nufin tabbatar da Æ´anci ga majalisar jiha tare da yin duba ga ayyukan zartarwa da kuma É—ora alhakin ci gaban al’umma ga gwamnati.

Kudirin dokar shugaban da ya ba ƴan majalisar dokoki da ɓangaren jihohi cin gashin kai ya samo asali ne tun daga majalisa ta 8, inda shugaban ƙasar daga baya ya kafa kwamiti da ya ba shi shawarwarin aiwatar da shi.

Majalisar ta yi gyara ne ga kundin tsarin mulki na Najeriya, inda aka ba majalisar dokoki da É“angaren shari’a na jihohi cin gashin kai, yayin da yanzu za a dinga sa kuÉ—aÉ—ensu cikin kasafin kudi na jiha.

Honorabul Aminu Shehu Shagari, tsohon Shugaban Kwamitin Shari’a ne a Majalisar Wakilai kuma shi ne ya gabatar da buÆ™atar da ta kai ga kafa dokar kuma mamba a kwamitin da shugaban Æ™asa ya kafa, ya shaida wa BBC cewa sun yi nazari kan dokar.

Ya ƙara da cewa sun yi hakan ne saboda yadda dimokuradiya ke tafiya a jihohi ba kamar yadda ake bukata ba.

Ya ce dimokuradiyya ba za ta tafi yadda ake so ba idan sai dukkanin ɓangarorin tafiyar da gwamnati sun dogara da gwamnati kafin iya aiwatar da duk wani abin da suke buƙata.

A cewarsa, wani muhimmin É“angare na dokar shi ne, dukkanin É“angarorin gwamnati za su zauna su tsara kasafin kuÉ—insu, za su kuma san abin da jihar ta ke da shi da abin da babu.

“Duk abin da majalisa ta ke son ta zartar za ta yi kan duk wani abin da Æ´an majalisar ke ganin al’umma za su amfana. Haka É“angaren shari’a na jihohi zai iya yanke hukunci yadda ya kamata ba tare da wani shakku ba,” in ji shi.

Sannan ya ce yanzu É“angarorin za su san nawa ko wane É“angare ke kashewa musamman wajen biyan albashi da kuma kuÉ—aÉ—en alawus na ‘Æ´an majlisar da masu taimaka masu da kuma kuÉ—aÉ—en kula da tafiyar da ofis.

Hakkin mallakar hoto
Buhari Sallau

Image caption

Buhari ya ba ‘Æ´an majalisar dokoki da kotuna ‘Æ´ancin cin gashin kai

Yanzu babu hannun gwamnonin kan abin da Æ´an majalisar dokokin za su kashe, wanda hakan zai sa majalisar aiwatar da aikinta ba wani shakku.

Dokar na nufin tabbatar da ‘Æ´anci ga majalisar jiha tare da yin duba ga ayyukan zartarwa da kuma É—ora alhakin ci gaban al’umma ga gwamnati.

Yadda gwamnonin suka fito suna adawa da ba majalisar dokoki da É“angaren shari’a na jihohi cin gashin kai, ana ganin za su iya Æ™alubalantar matakin a gaban kotu.

Honarabul Aminu ya ce gwamnonin na iya zuwa kotu, kuma kotu za ta iya kawo tsaiku idan ta ce a jira, kuma za a iya É—aukar lokaci ba a cimma nasarar abin da ake son cimma wa ba.

Ya ce kamar yadda kwamitin shugaban ƙasa ya bayar da shawara, ya kamata a zauna da kowace jiha a ji ƙorafinta a shata yadda ya kamata tsakanin kakakin majalisa da kuma gwamna.

More News

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...