Matashi ya mayar da naira miliyan 15 wa fasinjan da ya manta su a a-daidaita-sahunsa

Wani matashi mai suna Auwalu Salisu dan shekara 22, ya mayar da naira miliyan 15 da wani fasinja ya manta da shi.

Fasinjan dai ya zo ne daga kasar Chadi don sayen kaya a Kano sai kuma ya manta da shi.

Salisu wani mazaunin Yankaba da ke karamar hukumar Nasarawa a cikin babban birnin jihar, ya mayar da kudin ne bayan ya ji sakon bacewar kudin a wani gidan rediyo da ke Kano.

Kudaden wadanda sun kai maira miliyan 15 idan aka canza su, sun hada da; CFA miliyan 10.130 da kuma Naira miliyan 2.9.

Da yake zantawa da gidan rediyon Arewa a Kano, ya ce bai lura fasinjan nasa ya manta da kudin ba har ya isa gida.

Ya ce bayan gano kudin ne ya sanar da iyayensa wadanda suka umarce shi da ya je ya nemo mai shi.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon É—an majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...