
Rundunar ƴan sandan jihar Borno ta sanar da mutuwar , Abubakar A. Balteh mataimakin kwamishinan yan sanda na jihar wanda ya mutu a ranar Asabar sakamakon wani mummunan hatsarin mota.
Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar, ASP Nahum Kenneth Daso ne ya bayyana haka a cikin wani sako da ya wallafa a shafin sa na X .
Nahum ya bayyana rasuwar Balteh a matsayin wani babban rashi mai ciwo ga rundunar yan sandan Najeriya da kuma rundunar yan sandan jihar Borno.
Kafin rasuwar marigayin shi ne ke rikon muƙamin shugaban sashen binciken manyan laifuka na rundunar yan sandan jihar.

