A ranar Alhamis ne wata kotun majistare da ke Ogudu a jihar Legas ta bayar da belin wani ma’aikaci da ya daba wa manajan gidan karuwai wuka a kan kudi N200,000.
An tuhumi masinjan dan shekara 24, Huzairu Shehu, wanda ke zaune a unguwar Gengere da ke Mile 12 Ketu, jihar Legas da laifin haddasa mummunar barna.
Sai dai ya ki amsa laifin da ake tuhumarsa da shi. Alkalin kotun, Mrs M.O. Tanimola, ya kuma umurci wanda ake kara da cewa ya gabatar da mutum biyu da za su tsaya masa.
Ta ɗage ci gaba da sauraron karar har sai ranar 18 ga watan Oktoba. Tun da farko, mai gabatar da kara, Insp Donjiur Perezi, ya shaida wa kotun cewa wanda ake tuhuma ya aikata laifin ne a ranar 26 ga watan Satumba a Gengere.