Maniyyata Daga Nasarawa Da Za Su Je Hajji A Jirgin Farko Sun Yi Hatsari

Alhazan jihar Nasarawa da dama ne suka tsallake rijiya da baya a lokacin da motar da suke ciki tayi hatsari.

Motar maniyyatan ta yi hatsari ne a ranar Laraba a kan hanyarsu ta zuwa Abuja inda za su hau jirgin farko a rana Alhamis.

Hatsarin da ya ritsa da bas mai daukar mutum 18 da suke ciki ne a yankin Kara da ke Karamar Hukumar Keffi ta Jihar Nasarawa.

Da dama daga cikin maniyatan sun jikkata amma ba a samu asarar rayuka ba.

More from this stream

Recomended