Man City za ta san makomarta a Champions League ran Litinin

Manchester City's Etihad Stadium

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Manchester City ta buga gasar Zakarun Turai ta Uefa sau 10 ba ta taba lashe kofin ba

Ranar Litinin Manchester City za ta san makomarta a gasar Zakarun Turai, bayan daukaka kara da ta shigar kan dakatar da ita kaka biyu da UEFA ta yi.

City ta daukaka kara zuwa kotun sauraren kararrakin wasanni ta duniya, (Cas,) bayan da hukumar kwallon kafa ta Turai ta hukunta kungiyar ta Etihad.

Uefa ta ce ta samu City da karya dokokinta da dama ciki har da ta kashe kudade ba bisa ka’ida ba tsakanin 2012 zuwa 16.

Haka kuma an ci tarar Manchester City fam miliyan 25.

Tun da hukumar kwallon kafa ta Turai ta yanke wa City hukuncin, kungiyar ta ce za ta daukaka kara ga kotun sauraren kararrakin wasanni ta duniya.

A cikin watan Juni aka saurari daukaka karar da City ta shigar, inda Alkalan suka ji bahasin City da na Uefa ta fasahar bidiyo, amma a asirce.

Idan har City ba ta yi nasara ba, to ba za ta shiga gasar Zakarun Turai ta badi ba, sannan ba za ta fafata a Uefa Super Cup a gaba ba, koda ta lashe Champions League na bana.

City za ta karbi bakuncin Real Madrid a Etihad a wasa na biyu na kungiyoyi 16 da ke gasar Champions League ranar 7 ko kuma 8 ga watan Agusta.

Kungiyar ta Etihad ta yi nasarar doke Real Madrid da ci 2-1 a wasan farko da suka yi a Madrid, idan ta yi nasarar kai wa zagayen gaba za ta kara da Juventus ko kuma Lyon a wasan Quarter finals a Lisbon.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...