Manchester City ta samu nasarar zuwa zagaye na biyar a gasar FA bayan ta lallasa Burnley ci 5-0.
Gabriel Jesus da Bernardo Silva da Kevin de Bruyne da Sergio Aguero ne suka ci wa City kwallayen a ragar Burnley.
Pep Guardiola wanda ya lashe wa City kofin Premier da Carabao a bara, yana harin lashe kofi hudu a kakar bana.
Manchester City za ta hadu da Chelsea a wasan karshe na kofin Carabao, sannan za ta hadu da Schalke a zagaye na biyu a gasar zakarun Turai.
City da ke matsayi na biyu a teburin Premier, tazarar maki hudu ne ya raba ta da Liverpool da ke jan ragamar teburin, kuma ga shi yanzu ta kai zagaye na gaba a gasar FA.
City ta ci kwallaye 30 a wasanni bakwai da ta buga a 2019.