Majalisar wakilai ta nemi gwamnatin tarayya ta janye hanin da ta yi na sayar da mai a gidajen man dake garuruwan bakin boda

Majalisar wakilai ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta janye hanin da tayi na hana sayar da man fetur a garuruwan da suke da tazarar kilimita 20 daga kan iyakar Najeriya.

Majalisar ta zartar da matakin ne a ranar Talata biyo bayan kudirin da dan majalisa daga jihar Ogun, Adeboyega Isiaka ya gabatar.

Yan majalisar sun yi kira da hukumar kwastam ta Najeriya da kuma sauran hukumomin gwamnati da abin ya shafa da su kyale gidajen mai da suke a garuruwan kan iyaka kuma suke da cikakkiyar rijista a rika kai musu.

A shekarar 2019 gwamnatin tsohon shugaban kasa, Muhammad Buhari ta hana kai mai a duk wani gidan mai dake da tazarar kilimita 20 daga boda.

Gwamnatin ta bayar da umarnin ne a lokacin domin dakile fasa kwaurin man fetur da ake zuwa kasashe makota irin su Nijar, Kamaru, Benin Chad da kuma Togo.

More News

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...