Majalisar dokokin Zamfara ta tsige kakakinta saboda tsanantar rashin tsaro a jihar

Majalisar dokokin jihar Zamfara ta tsige kakakinta, Bilyaminu Moriki, tare da nada Bashar Gummi, a matsayin kakakin majalisar.

Hakan ya biyo bayan kudirin da dan majalisa mai wakiltar mazabar Maru, Nasiru Abdullahi ya gabatar, inda mambobi 18 cikin 24 suka amince da shi.

Mambobin majalisar 18 daga cikin 24 sun amince da tsige kakakin yayin wani taron gaggawa da suka gudanar a daren Alhamis.

A cewar ‘yan majalisar, an dakatar da shugaban majalisar ne saboda kalubalen tsaro da ya addabi jihar ba tare da wani yunkuri da majalisar ta yi na dakatar da wannan barnar ba.

Mambobin sun bukaci shugaban majalisar da aka nada da ya yi amfani da mukaminsa wajen kawo karshen ‘yan fashi da suka kai ruwa rana. 

Daya daga cikin ‘yan majalisar, Shamsudeen Basko, mai wakiltar mazabar Talata Mafara, ya shaida wa mai goyon bayan shugaban majalisar cewa, batun rashin tsaro na daya daga cikin muhimman batutuwan da ya kamata a baiwa fifiko wanda ya kai ga dakatar da tsohon kakakin.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...