Majalisar dokokin Zamfara ta tsige kakakinta saboda tsanantar rashin tsaro a jihar

Majalisar dokokin jihar Zamfara ta tsige kakakinta, Bilyaminu Moriki, tare da nada Bashar Gummi, a matsayin kakakin majalisar.

Hakan ya biyo bayan kudirin da dan majalisa mai wakiltar mazabar Maru, Nasiru Abdullahi ya gabatar, inda mambobi 18 cikin 24 suka amince da shi.

Mambobin majalisar 18 daga cikin 24 sun amince da tsige kakakin yayin wani taron gaggawa da suka gudanar a daren Alhamis.

A cewar ‘yan majalisar, an dakatar da shugaban majalisar ne saboda kalubalen tsaro da ya addabi jihar ba tare da wani yunkuri da majalisar ta yi na dakatar da wannan barnar ba.

Mambobin sun bukaci shugaban majalisar da aka nada da ya yi amfani da mukaminsa wajen kawo karshen ‘yan fashi da suka kai ruwa rana. 

Daya daga cikin ‘yan majalisar, Shamsudeen Basko, mai wakiltar mazabar Talata Mafara, ya shaida wa mai goyon bayan shugaban majalisar cewa, batun rashin tsaro na daya daga cikin muhimman batutuwan da ya kamata a baiwa fifiko wanda ya kai ga dakatar da tsohon kakakin.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...