Mai Shari’a Ayo Salami wanda ke shugabancin wannan kwamitin yayi tir da Allah wadai da, abin da ya kira labarin kanzon kurege da aka wallafa a cikin jaridu, wanda lauyoyin Ibrahim Magu ne suke cewa wai yayi juyayi da nadama a kan karban wannan shugabancin da aka bashi na kwamitin da ke binciken Ibrahim Magu.
Ayo Salami ya nuna mamakinsa kan yadda aka ari bakinsa aka ci masa albasa. Malam Nasiru Zahradin Æ™wararre a kan fafutukar yaÆ™i da cin hanci a Najeriya, ya ce, “Tun ba yau ba ake irin wannan buge-buge a jaridu, musamman irin jaridun nan na zamani, su suke bubbuga waÉ—annan labarai, mutane masu goyon bayansa da lauyoyi ‘yan’uwansa suke ta sawa a kafar yaÉ—a bayanai domin su ga wannan kwamiti da aka kafa sun wargaza shi, sun ce abunda yake ba daidai ne ba”
Ya Æ™ara da cewa ya kamata hukuma ta tanadi hukunci ga masu irin wannan cin zarafi ga al’umma. A gurfanar da su gaban shari’a. Ya ce su kan su, kafofin yaÉ—a labarai da aka ce sun yi ta Æ´aÉ—a labaran, wanda na kanzon kurege ne, su ma a hukunta su.
Abdulkarim Ibrahim wani Æ™wararre a harkar intanet da yadda ake amfani da ita wajen yaÆ™i da cin hanci, ya jinjina wa Ayo Salami. Ya ce suna so ne a janye labarin da kowa ya riga ya sani, bai dace ba a ce komai ya faru sai a kai shi ga jarida, al’umma basa sanin me ake ciki sai dai a yi ta surutai a jarida a haka har abun ya wuce.
A wancan lokacin, lauyoyin na ganin suna burge shi don haka ma suka cigaba da irin wannan aikin. Amma Ayo Salami ya fahimci manufarsu, kuma ya ƙaryata cewa bai faɗi magan nan ba.