Mahara Sun Kashe Sojoji Biyu Da Wasu Mutane 17 A Benue

Sojoji 2 da wasu mutane 15 aka bada rahoton an kashe a wani hari da wasu yan bindiga suka kai kan wasu ƙauyuka uku dake karamar hukumar Apa ta jihar Benue.

Mazauna yankin sun bayyana cewa an kai harin ne a tare lokaci guda da misalin karfe 06:00 na yammacin ranar Talata kan ƙauyukan Opaha, Odogbo da kuma Edikwu dake karamar hukumar ta Apa.

Wani mazaunin yankin da ya bayyana sunansa da Kole ya ce gawarwaki 17 aka gano a cikin daji ciki har da sojoji biyu na rundunar Operation Whirl Stroke lokacin da jami’an tsaro suke bincike a yankin da asubahin ranar Laraba.

Har ila ya bayyana cewa ɗaya daga cikin gawar sojojin ta kwamandan rukunin sojojin ne da suka yi kokarin dakile farmakin da maharan suka kawo.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]