Mafi Yawan Masu Corona Basa Yarda Suna Da Cutar – Ministan Lafiya – AREWA News

Ministan kiwon Lafiya, Osagie Ehanire, ya bayyana cewa mafi yawan masu cutar Coronavirus babu wata alama a jikin su mai nuna su na dauke da ciwon.

“Kashi 80 bisa 100 na masu dauke da cutar Coronavirus a kasar nan, babu alamar da ke nuna cutar a jikin su.

“Dalili da yasa yake da wahalar gaske mu gamsar da su cewa akwai cutar a jikin su.

“Ko ka yi kokarin nuna musu ba za su amince da kai ba.Saboda su na jin garau a jikin su, amma kuma a talbijin su na ganin yadda ake nuno masu cutar ranga-ranga. Kuma su na ganin irin yadda suke mutu kwakwai rai kwakawai a Cibiyoyin Kula da Masu Cutar.

“Wasu kuma da sun ji su na da cutar, ba su jira a killace su sai kawai su tsere ko su boye, a neme su a rasa.

Da yawa su na guje wa killacewa.

Rahotanni da dama daga jihohi sun tabbatar da wasu kuma sun tsere daga inda ake killace da su.” Inji Ehanire.

Masu dauke da Cutar da dama sun tsere a Kano, Lagos, Gombe da sauran jihohi da yawa.

Wani likita Mai suna John Oghenehero, ya ce mutane na gudun killacewa ne saboda gani suke yi kamar an yi wa rayuwar su wani bakin tambari.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...