Mabiya a jihohi da dama sun gudanar da zanga-zangar kisan Khamenei

Mambobin ƙungiyar ƴan uwa musulmi ta Najeriya da aka fi sani da shia sun gudanar da zanga-zangar lumana a jihohi da dama kan kisan jagoran addinin ƙasar Iran, Ayatullah Ali Khamenei.

An kashe Khamenei ni ne  a wani farmaki na haɗin gwiwa da Amurka da Isra’ila su ka kai a ranar Asabar.

Anga masu zanga-zangar a jihohin Lagos,Kano, Niger, Sokoto, Gombe da kuma Kaduna suna allawadai da harin da Amurka da Isra’ila su ka da ya yi sanadiyar mutuwar Khamenei tare da wasu daga cikin iyalansa.

Akwai rahoton makamanciyar irin zanga-zangar a jihohi Bauchi da Yobe.

Masu zanga-zangar sun rika daga tutar kasar Iran tare da hoton Khamenei da kuma wasu allunan kwali dake nuna adawa da kasar Isra’ila da kuma Amurka.

Zanga-zangar na zuwa ne dai-dai lokacin da ake cigaba da zafafa kai hare-hare a tsakanin Amurka,Isra’ila da kuma Iran.

More from this stream

Recomended