Lionel Messi: Ta faru ta kare: zakaran kwallon kafa na duniya zai bar Barcelona

Lionel Messi

Zakaran kwallon kafar duniya Lionel Messi ya ce zai bar Barcelona, bayan share kimanin shekarar 20 yana taka leda a kungiyar.

Kungiyar ta tabbatarwa da kamfanin dillancin labarai na AP a ranar Talata cewa dan wasan Argentinan ya aika mata da wani bayani a rubuce dake bayyana yunkurinsa na barin kungiyar.

Wannan sanarwar na zuwa ne kwana 11 bayan ragargazar da Munich ta yi wa Barcelona da ci 8-2 a wasan daf da kusa da na karshe a gasar zakarun Turai, wanda wannan daya ne daga cikin wulakancin kwallon da dan wasan ya gani a tarihin rayuwarsa.

Messi wanda ya lashe kyautar Ballon d’O har sau shida ya fara takawa Barce leda ne a 2004, kuma ya lashe gasar zakarun Turai har sau hudu.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...