Bola Ahmad Tinubu zaÉ“aÉ“É“en shugaban kasa da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso É—an takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP a zaÉ“en shugaban kasa na 2023 sun yi wata ganawa ta tsawon sa’o’i 4 a birnin Paris na kasar Faransa.
A cewar jaridar The Cable da ta rawaito labarin, ta ce ganawar ta mayar da hankali ne kan batun jawo hankalin Kwankwaso ya shiga cikin gwamnatin Tinubu da za a kafa a ranar 29 ga watan Mayu.
Tun bayan lashe zaben Tinubu ya nuna sha’awarsa ta kafa gwamnatin hadin kan kasa ta hanyar bawa Æ´an adawa wasu mukamai a gwamnatinsa.
Ganawar ta kuma mayar da hankali kan zaɓen shugabannin majalisar kasa ta 10 da za a kaddamar a watan Yuni.
Ganawar ta birnin Paris ta fara ne da misalin 12:30 na rana zuwa 04:45 na rana.
Ganawar ta kuma samu halartar Femi Gbajabiamila wanda ake tunanin shi ne zai zama shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa a gwamnatin Tinubu da kuma Abdulumumin Jinin Kofa wanda yake tare da Kwankwaso.