Hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Niger ta ce wani jirgin ruwa dake ɗauke da mutane 22 ya kife a karamar hukumar Agwara ta jihar.
Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ya rawaito,Salihu Garba shugaban hukumar na cewa jirgin ya dauko fasinjoji daga kauyen Kasabo na karamar hukumar Agwara ya zuwa garin Yauri na jihar Kebbi.
Garba ya ce hatsarin ya faru da misalin karfe 10 zuwa 12 na ranar Litinin.
Ya ce hatsarin ya faru ne ranar da kasuwar Yauri take ci ya kara da cewa ma’aikatan ceto sun gaza ceto ko ɗaya daga cikin fasinjojin.
Ya kuma kara da cewa torokon ruwa mai karfi ne musabbabin hatsarin.