Kungiyoyin ƙwadago za su fara yajin aiki ranar 8 ga watan Nuwamba kan cin zarafin Ajaero

Gamayyar kungiyoyin ƙwadago sun shirya shiga yajin aiki a ranar 8 ga watan Nuwamba kan yadda akaci zarafin shugaban kungiyar NLC, Kwamared Joe Ajaero.

Haɗakar kungiyar ƙwadago ta NLC da TUC sun gudanar da wani taron manema labarai a ranar Juma’a kan abin da ya faru a jihar Imo.

A ranar Laraba ne aka rawaito wasu jami’an tsaro sun yi awon gaba da Ajaero a hedikwatar kungiyar ta NLC dake Owerri.

Kungiyar NLC ta ce an lakada masa duka lokacin da yake hannun jami’an tsaro zargin da rundunar yan sandan jihar ta musalta inda ta ce wasu batagari ne suka dake shi amma jjami’an yan sandan su ka samu nasarar ceto shi.

A yayin ta taron manema labaran shugabannin ƙwadagon sun yi kira da a binciki kwamishinan yan sandan jihar Imo, Ahmad Barde kana a ɗauke shi daga jihar.

Shugabannin kungiyar sun kuma yi kira da a kama tare da hukunta Nwaneri Chinasa wani mai taimakawa gwamnan jihar da ake zargi jagoranta yan ta’addar da suka kai wa yan kungiyar da kuma ma’aikata farmaki.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...