Kungiyar Æ™wadago ta NLC ta umarci ma’aikata da su koma bakin aiki bayan kammala yajin aiki na kwanaki biyu.
Kungiyar cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Laraba ta umarci mambobinta dake kasa baki daya da su koma aiki ranar Alhamis.
Yajin aikin ya fara ne a ranar Talata biyo bayan umarnin shiga yajin aikin da kungiyar ta NLC ta bayar a ranar Juma’a.
Shugaban kungiyar ta NLC Joe Ajaero ya yabawa sauran kungiyoyin ma’aikata da suka bi umarnin shiga yajin aikin.