Kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen Jihar Neja ta nuna alhini da jimami kan mummunar ambaliyar da ta afkawa al’ummomin Mokwa, inda ta mika sakon ta’aziyya da goyon baya ga dukkan iyalan da abin ya shafa.
Shugaban CAN na jihar, Mai Alfarma Reverend Dokta Bulus Dauwa Yohanna, wanda kuma shi ne Bishop na Katolika a Diocese na Kontagora, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi. Ya ce suna addu’a tare da nuna goyon baya daga daukacin al’ummar Kirista a jihar.
“Na mika sakon ta’aziyyar mu ga iyalan da suka rasa ‘yan uwansu da duk wanda wannan bala’i ya shafa. Muna tare da ku a wannan lokaci mai cike da jaraba,” in ji shi.
Bishop Yohanna ya yaba da matakin da gwamnatin tarayya da ta jihar suka dauka na umurtar hukumomin da abin ya shafa da kuma hukumomin agaji da su gaggauta kai dauki ga mutanen da ambaliyar ta shafa.
Ya kuma bukaci mazauna yankin da su kasance masu juriya da fatan alheri domin samun damar farfadowa daga wannan annoba cikin karfi da nufin ci gaba.
“Yayin da muke ci gaba da yi muku addu’a, muna kuma kira da ku ci gaba da kasancewa da fata da kwarin gwiwa,” in ji Bishop din.
Kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) Ta Aika Da Ta’aziyya Ga Al’ummar da Ambaliya Ta Shafa A Neja
