Kungiyar CAN ta nemi a gudanar da bincike kan ruftawar masallacin Zariya

Kungiyar Kiristoci ta Najeriya CAN tayi kira ga gwamnatin jihar Kaduna da kuma ta tarayya da su binciki dalilin rugujewar wani bangare na babban masallacin Juma’a na Zaria.

Shugaban kungiyar CAN, Daniel Okoh shi ne yayi wannan kira a cikin wani sakon ta’aziyya ga al’ummar Musulmin Zaria.

A cikin sanarwar da aka fitar a Abuja Okoh ya ce binciken zai taimaka wajen kare faruwar irin haka anan gaba kana yayi kira ga gwamnati ta tabbatar da ta samar da kariya a wuraren ibada.

Okoh ya bayyana tausayinsa da jimaminsa ga al’ummar musulmi dama gwamnatin jihar inda yayi addu’ar juriya ga iyalan wadanda suka mutu.

Mutane da dama ne dai suka mutu bayan da wani sashe na ginin masallacin ya ruguzo lokacin da ake tsaka da sallar Juma’a.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon É—an majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...