Kotun Kolin Najeriya Za Ta Yanke Hukuncin Zaɓen Shugaban Ƙasa Ranar Alhamis

Kotun Koli ta saka ranar Alhamis domin yanke hukunci kan daukaka karar da Atiku Abubakar ɗan takarar shugaban kasa a jam’iyar PDP a zaɓen da ya wuce da kuma Peter Obi na jam’iyar LP suka shigar gabanta.

Atiku da Obi na kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Faburairu da ya bawa, Bola Ahmad Tinubu na jam’iyar APC nasara.

Daraktan yaɗa labarai kotun, Dr Festus Akande shi ne ya tabbatar da haka a ranar Laraba,

A ranar 9 ga watan Satumba ne kotun sauraron kararrakin zaɓen shugaban ƙasa ta kori karar da ƴan takarar biyu suka shigar saboda rashin hujjoji.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...