
Kotun daukaka kara dake Abuja ta tabbatar da hukuncin da kotun sauraren karar zaben gwamnan jihar Edo ta yanke da ya tabbatar da zaben, Monday Okphebolo na jam’iyar APC a matsayin gwamnan jihar.
Da take tabbatar da hukuncin rukunin alkalan kotun daukaka karar su uku sun yi watsi da daukaka karar da jam’iyar PDP da dantakararta Asue Ighadolo suka yi.
Mohammed Danjuma wanda ya karanta hukuncin kotun a madadin sauran alkalan ya ce daukaka karar ba shi da tushe bare makama.
Danjuma ya ce jam’iyar PDP da Ighadolo dukkaninsu sun gaza tabbatar da ikirarin cewa kotun sauraren kararrakin zaben tayi kuskure da tabbatar da zaben da aka yi wa Okphebolo.
Amma kuma kotun daukaka karar ta ce kotun sauraren kararrakin zaben tayi kuskure da ta amince da injinan BVAS na tantance masu kada kuri’a da ta amince da su a matsayin sheda da masu kara suka gabatar da ita.
A saboda haka kotun ta cire injinan BVAS 133 da aka gabatar a matsayin sheda da masu kara suka gabatar.