A farkon shekarar nan babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yankewa Maryam hukuncin kisa bayan da ta same ta da laifin kashe mijinta Bilyaminu Bello, da ga tsohon shugaban jam’iyyar PDP a Najeriya.
Alkalan kotun uku da suka saurari shari’ar, sun ce hujjojin da Maryam ta gabatar na kare kanta ba su da tushe balle makama.
Ita dai wacce ake tuhumar, wacce suke da ‘ya’ya biyu da marigayin, ta ce Bilyaminu ya fada ne akan madaukin shisha abin da ya yi sanadin mutuwarsa.
Lamarin ya faru ne shekarar 2017 bayan da ma’auratan suka samu sabani a tsakaninsu.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito lauyoyin Maryam suna cewa za su daukaka kara zuwa kotun kolin kasar.