Kotun Ƙoli ba ta bayyana hukuncin da ta yanke kan taƙaddamar zaɓen gwamnan Sokoto ba

A ranar Laraba ne kotun koli ta ɗage hukunci a karar da jam’iyyar PDP da dan takararta, Sa’idu Umar suka shigar kan zaben gwamnan jihar Sakkwato, Ahmad Aliyu.

Kwamitin mutum biyar karkashin jagorancin mai shari’a Kudirat Kekere-Ekun ta dage ci gaba da sauraron karar bayan sauraron bahasi daga bangarorin da ke da hannu a cikin karar.

Sai dai kotun daukaka kara da ke Abuja, ta tabbatar da zaben Aliyu.

Umar da PDP sun yi zargin cewa Aliyu da mataimakinsa Idris Gobir ba su cancanci tsayawa takarar gwamna ba.

Sun kuma yi zargin cewa zaben ba wai kawai an tafka kura-kurai ba ne, ba a ma gudanar da shi bisa ka’idojin da dokar zabe ta 2022 ta tanada ba.

Kotun daukaka kara, duk da haka, ta yi watsi da daukaka karar da suka yi saboda rashin cancanta.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...