Kotu ta yi watsi da ƙarar Binani, ta tabbatar da Fintiri a matsayin halattaccen gwamnan Adamawa

Kotun daukaka kara da ke Abuja a ranar Litinin ta yi watsi da karar da jam’iyyar APC da ‘yar takarar gwamna, Sanata Aisha Dahiru Binani, suka shigar na neman a soke zaben Umar Ahmadu Fintiri a matsayin zababben gwamnan jihar Adamawa.

Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da hukuncin kotun sauraren kararrakin zaben gwamnan jihar Adamawa wacce tun farko ta ayyana Gwamna Fintiri na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben.

Hukuncin da Mai Shari’a Tunde Oyebanji Awotoye ya rubuta ya yi watsi da shari’ar Binani da APC bisa wasu dalilai na rashin ka hankali.

Daga cikin dalilan, Kotun daukaka kara ta bayyana cewa Binani da APC sun kasa kiran wakilan zabe da suka halarci zaben a matsayin shedu amma abin takaici sun kira ko’odinetoci na yakin neman zabe wadanda ba sa nan a wurin zaben.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...