Kotu ta yanke wa likita hukuncin ɗaurin rai-da-rai saboda laifin fyaɗe

Kotun laifukan lalata da cin zarafin cikin gida a jihar Legas da ke zamanta a Ikeja a ranar Talata ta yanke hukuncin daurin rai-da-rai ga daraktan kula da lafiya na gidauniyar kula da cutar daji, Dakta Olufemi Olaleye, bisa laifin lalata da ‘yar uwar matarsa.

Mai shari’a Rahman Oshodi ya yanke masa hukuncin ne bayan ya same shi da laifin lalata da wata yarinya ‘yar shekara 15.

Alkalin kotun ya ce masu gabatar da kara sun iya tabbatar da karar ba tare da wata shakka ba, kuma dukkan shaidun da ke gaban kotun sun tabbatar.

An gurfanar da Olaleye ne a kan laifuka biyu da suka shafi lalata da kuma cin zarafi ta hanyar lalata da ‘yar uwar matarsa.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...