Kotu ta yanke wa likita hukuncin ɗaurin rai-da-rai saboda laifin fyaɗe

Kotun laifukan lalata da cin zarafin cikin gida a jihar Legas da ke zamanta a Ikeja a ranar Talata ta yanke hukuncin daurin rai-da-rai ga daraktan kula da lafiya na gidauniyar kula da cutar daji, Dakta Olufemi Olaleye, bisa laifin lalata da ‘yar uwar matarsa.

Mai shari’a Rahman Oshodi ya yanke masa hukuncin ne bayan ya same shi da laifin lalata da wata yarinya ‘yar shekara 15.

Alkalin kotun ya ce masu gabatar da kara sun iya tabbatar da karar ba tare da wata shakka ba, kuma dukkan shaidun da ke gaban kotun sun tabbatar.

An gurfanar da Olaleye ne a kan laifuka biyu da suka shafi lalata da kuma cin zarafi ta hanyar lalata da ‘yar uwar matarsa.

More News

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...