Kotu ta umarci gwamnatin tarayya da ta kayyade farashin kayayyaki a Najeriya

A ranar Laraba ne wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Legas ta umarci gwamnatin tarayya da ta tsayar da farashin kayayyaki da na man fetur cikin kwanaki bakwai.

Mai shari’a Ambrose Lewis-Allagoa ya umarci gwamnati da ta gyara farashin madara, fulawa, gishiri, sukari, kekuna, da kayayyakinsu, ashana, babura da kayayyakinsu, motoci da kayan aikinsu da kuma kayayyakin man fetur, wanda ya hada da dizal, da kananzir.

Alkalin ya bayar da umarnin ne a lokacin da yake yanke hukunci a wata kara mai lamba FHC/L/CS/869/2023 da mai rajin kare hakkin dan Adam, Mista Femi Falana, ya shigar a kan hukumar kula da farashin kayayyaki da kuma babban lauyan gwamnatin tarayya, wanda aka lissafa a matsayin wadanda ake tuhuma na daya da na biyu.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]